Iran ta sake sabon gargadi akan kasar Amurka da Isra’ila mai zafin gaske

IMG 140730 17826 1786972088040

Mataimakin shugaban harkokin siyasa na dakarun juyin juya halin Iran, Yadollah Javani, ya ce matakan da Iran ke ɗauka a yaƙin da ake yi a halin yanzu na kare kai ne, amma za su iya komawa na kai hare-hare a gaba.

Da yake magana a wata hira da gidan talabijin da rediyon ƙasar Iran, Javani ya ce maƙiyan Iran ne suka fara yaƙin, kuma martanin Iran ya kasance na kare kanta.

Iran ta kuma ce za ta ɗauki duk matakin da ya dace domin kare ƙasar da kuma daƙile barazanar maƙiya, tare da yiwuwar sauya salon martaninta idan lamarin ya buƙaci hakan.

Ya ce rundunonin sojin Iran za su ɗauki sabbin matakai bisa umarnin da aka bayar, tare da ɗaukar duk wani mataki da ya dace don kare ƙasar, tabbatar da tsaro da kuma dakile barazanar maƙiya a lokacin da ya dace.

Kalaman Javani na zuwa ne bayan mai bai wa babban kwamandan IRGC shawara, Mohammad Reza Naqdi, ya bayyana cewa Iran ta yanke shawarar sauya aƙidar soja daga ta kare kai zuwa wadda ta haɗa da kai hare-hare idan an ga hakan ya zama dole.

BBC

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *