Ibtila’i: Mahalarta Ɗaurin Aure 19 Daga Jihar Kano Sun Rasu A Hatsarin Mota A Filato !

FB IMG 1736861826367

Wasu mutum 19 daga Jihar Kano sun rasa rayukansu a wani mummunan hatsarin mota a yankin Kwanar Maciji da ke Ƙaramar Hukumar Pankshin, a Jihar Filato.

Shugaban Ƙaramar Hukumar, John Dasar, ya bayyana cewa motar ta kama da wuta ne yayin da mutanen ke kan hanyar komawa gida daga ɗaurin aure da aka yi a Ƙaramar Hukumar Barikin Ladi ranar Asabar.

A cewarsa, an ceto mutum 11 ciki har da direban motar da wasu fasinjoji, amma sun ji munanan raunuka.

Sauran fasinjoji 19 sun ƙone ƙurmus har ba a iya gane su.

An garzaya da waɗanda suka tsira da ransu zuwa Babban Asibitin Pankshin, inda ake ba su kulawar gaggawa.

Domin samun sauran shirye shiryenmu zaku iya biyo mu ta wannan shafukan👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *